• Home  
  • Za A Yi Zaɓen Kananan Hukumomin Kano A Oktoba
- Babban Labari - Labarai

Za A Yi Zaɓen Kananan Hukumomin Kano A Oktoba

Hukumar zaɓe ta jihar Kano, KANSIEC, ta matso da zaɓen ƙananan hukumomi 44 da a baya ta tsara yi ranar 30 ga watan Nuwamba, 2024, zuwa ranar 26, ga watan Oktoba, 2024.

ABBA KABIR YUSUF

Hukumar zaɓe ta jihar Kano, KANSIEC, ta matso da zaɓen ƙananan hukumomi 44 da a baya ta tsara yi ranar 30 ga watan Nuwamba, 2024, zuwa ranar 26, ga watan Oktoba, 2024.

Wannan bayani na ƙunshe a jawabin da shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan ya yi wani taron manema labarai, a yau Juma’a a hedikwatar hukumar da ke birnin dabo.

Shugaban hukumar ya ce sun yi hakan ne domin biyayya ga hukuncin Kotun Ƙoli ta Najeriya. 

Kotun ƙoli ta Najeriya dai ta bayar da wa’adin watan Oktoba domin tabbatar da cin gashin kai na ƙananan hukumomi.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000