Ana hasashen yiwuwar rikici tsakanin Amurka da Iran

Ana ci gaba da nuna damuwa kan yiwuwar sake barkewar rikici tsakanin Amurka da Iran, bayan da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana rashin gamsuwarsa da bukatun da Iran ta gabatar a tattaunawar da ke gudana.

Wani babban jami’in soja a Iran ya yi gargadin cewa akwai yiwuwar sabon rikici ya ɓarke, yana mai cewa halin da ake ciki na iya rikidewa idan ba a samu matsaya ba.

Rahotanni daga kafafen yada labarai na Iran sun ce Tehran ta gabatar da wani sabon daftari ga Pakistan, wadda ke taka rawa a matsayin mai shiga tsakani, sai dai ba a bayyana cikakken bayani kan abin da daftarin ya kunsa ba.

Post masu alaƙa

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM

Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu

Kwankwaso da Obi za su fice daga ADC