Fursunoni tara da ke zaman kaso a Gidan Gyaran Hali na Tsaka-tsaki da ke Wudil a Jihar Kano sun samu nasarar kammala haddar Alƙur’ani Mai Tsarki.
Wannan gagarumar nasara ta zo daidai da bikin cika shekaru 50 da kafuwar gidan gyaran halin.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali tA Najeriya reshen Jihar Kano, CSC Musbahu Lawan Kofar Nasarawa, ya bayyana cewa wasu daga cikin fursunonin ba su da cikakken ilimin karatun Alƙur’ani lokacin da aka kawo su gidan.
A cewarsa, ta hanyar jajircewa, ladabi da kuma ingantaccen tsari na koyarwa a gidan yarin, fursunonin sun samu nasarar haddace Alƙur’ani baki ɗaya. Kofar Nassarawa ya bayyana cewa hakan ya nuna tasirin shirye-shiryen gyaran hali na addini a cibiyar.
“Wannan nasara na nuna ƙoƙarin da hukumar ke yi na gyarawa, da farfaɗowa da kuma mayar da fursunoni cikin al’umma yadda doka ta tanada a Dokar Hukumar Gyran Hali ta 2019,” in ji shi.
Shugaban cibiyar Wudil, CSC Ibrahim Wada Ibrahim, ya bayyana cewa wannan nasara alama ce ta kyakkyawan shugabanci da jajircewa wajen bunƙasa rayuwar fursunoni. Ya gode wa rundunar jihar bisa goyon bayan da suka bayar, yana mai
Shugaban Jami’ar Aliko Dangote, Farfesa Musa Tukur Yakasai, ya yaba da ƙoƙarin rundunar wajen sauya rayuwar fursunoni, yana mai cewa irin waɗannan shirye-shirye na taimakawa wajen mayar da su ’yan ƙasa masu nagarta.
Ita ma, Shugaban Kwamitin Afuwa na Jihar Kano, Hajiya Azumi Namadi Bebeji, ta jaddada ƙudurin gwamnati na inganta jin daɗin fursunoni, tare da yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ci gaba da nuna tausayi da goyon baya ga fursunoni a dukkan cibiyoyin gyaran hali na jihar.
Ta taya fursunonin tara murna kan wannan nasara tare da ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da riƙe kyawawan halaye da ci gaban addini da suka samu. Sa’nnan ta buƙaci dukkan fursunoni da su ci gaba da yi wa Jihar Kano addu’ar zaman lafiya, ci gaba da wadata.
Konturolan Gyaran Hali na Jihar Kano, Ahmed Yusuf Lakpene, ya yaba wa Babban Konturola na Ƙasa, Sylvester Ndidi Nwakuche, bisa umarninsa na inganta shirye-shiryen ilimi da koyon sana’o’i a gidajen gyaran hali a faɗin ƙasa.
A cewarsa, irin waɗannan shirye-shirye na da matuƙar muhimmanci wajen bai wa fursunoni damar dogaro da kai da kuma sauƙaƙa dawowarsu cikin al’umma cikin nasara.