A Kawo Min Inda Na Ce Shiga Siyasa Haram Ne — Sheikh Pantami

Fitaccen malamin Musulunci Sheikh Isa Ali Pantami ya ƙalubalanci masu da’awar cewa a baya ya ce shiga siyasa haramun ne da su kawo shaidar abin da suke iƙirarin.

Sheikh Pantami wanda ya kasance tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, ya  jefa wannan ƙalubale ne bayan da ya bayyana aniyarsa ta neman tsayawa takarar kujerar Gwamna a Jihar Gombe.

Fitaccen malamin ya yi zargin cewa yawanci mutane sukan yanko wasu maganganunsa su haɗa da wasu su yaɗa, domin cimma wani burinsu.

Pantami ya bayyana haka ne yayin wata tattaunawa da BBC Hausa ya yi da shi, inda ya ce, ya shiga siyasa ne domin kawo shugabanci nagari a Najeriya.

A cewarsa tsohon ministan, mutane da dama ne suka fara kiran sa da ya fito takarar gwamna duk da yana ƙi a baya.

Ya ƙara da cewa amma a yanzu baya ga addu’o’i da neman yardar Allah an fara rinjayar sa

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda