Shugabannin Arewa Su Tattauna Matsalar Tsaro Da Shigowar Sojin Amurka — Farfesa Mansur

Shugaban riƙo na Majalisar Muslim Solidarity a Jihar Sakkwato, Farfesa Mansur Ibrahim Sa’id, ya ce lokaci ya yi da shugabannin Arewa za su haɗu domin tattauna yadda matsalar tsaro ke ƙara ƙamari a yankin.

Ya bayyana haka ne a taron shekara na majalisar da aka gudanar a Jami’ar Usmanu Danfodiyo a makon da ya gabata.

Ya ce halin da Arewa ke ciki ba zai bari a yi shiru ba, domin gudun kada matsalolin su ƙara ta’azzara.

A cewarsa, ya kamata shugabannin yankin su kira taro kan matsalar tsaro, shigowar sojojin Amurka, da kuma rikicin ƙabilanci.

Ya ƙara da cewa dole shugabanni su haɗa kai su yi magana da murya ɗaya don nemo mafita.

Farfesan, ya kuma buƙaci Gwamnatocin Tarayya da na jihohi su tallafa wa manoma, inda ya ce harkar noma na fuskantar matsala saboda tsadar kayan noma da kuma faɗuwar farashin amfanin gona.

Ya ce ya kamata gwamnati ta bai wa manoma kayan aiki ko tallafi, sannan ta riƙa sayen amfanin gonarsu a farashi mai kyau.

Dangane da kalaman uwargidan shugaban ƙasa kan batun hare-haren Amurka, Farfesan ya ce sun yi Allah-wadai da maganar, domin a ganinsu ba ta nuna goyon baya ga mutanen Arewa ba.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda