Rahotannin da ke fitowa daga jihar Kano sun nuna cewa an samu ƙarancin fitowar mutane zaɓukan cike gurbin wasu ƴan majalisar dokokin jihar biyu.
An gudanar da zaɓukan a rumfunan zaɓe 1,014 a faɗin ƙananan hukumomin Ungogo da Municipal.
Bayanai sun nuna cewa duk da isar jami’an zaɓe rumfunan a kan lokaci, da dama mutane sun ƙi fita zaɓukan.
Hukumar zaɓen ƙasar dai ba ta saka sunan jam’iyyar NNPP da ADC da PDP a kan takardar kaɗa ƙuri’a ba.
Kawo yanzu dai babu rahoton wani tashin hankali a zaɓukan.
Jami’an tsaro sun ƙarfafa tsaro a wuraren da ake gudanar da zaɓukan