An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen cike gurbi a Kano

Rahotannin da ke fitowa daga jihar Kano sun nuna cewa an samu ƙarancin fitowar mutane zaɓukan cike gurbin wasu ƴan majalisar dokokin jihar biyu.

An gudanar da zaɓukan a rumfunan zaɓe 1,014 a faɗin ƙananan hukumomin Ungogo da Municipal.

Bayanai sun nuna cewa duk da isar jami’an zaɓe rumfunan a kan lokaci, da dama mutane sun ƙi fita zaɓukan.

Hukumar zaɓen ƙasar dai ba ta saka sunan jam’iyyar NNPP da ADC da PDP a kan takardar kaɗa ƙuri’a ba.

Kawo yanzu dai babu rahoton wani tashin hankali a zaɓukan.

Jami’an tsaro sun ƙarfafa tsaro a wuraren da ake gudanar da zaɓukan

Post masu alaƙa

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC