An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen cike gurbi a Kano

Rahotannin da ke fitowa daga jihar Kano sun nuna cewa an samu ƙarancin fitowar mutane zaɓukan cike gurbin wasu ƴan majalisar dokokin jihar biyu.

An gudanar da zaɓukan a rumfunan zaɓe 1,014 a faɗin ƙananan hukumomin Ungogo da Municipal.

Bayanai sun nuna cewa duk da isar jami’an zaɓe rumfunan a kan lokaci, da dama mutane sun ƙi fita zaɓukan.

Hukumar zaɓen ƙasar dai ba ta saka sunan jam’iyyar NNPP da ADC da PDP a kan takardar kaɗa ƙuri’a ba.

Kawo yanzu dai babu rahoton wani tashin hankali a zaɓukan.

Jami’an tsaro sun ƙarfafa tsaro a wuraren da ake gudanar da zaɓukan

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda