Abin da Bala Kaura ya ce kan rade-radin sauya shekarsa zuwa APC

Yayin da ake ci gaba da lissafa gwamnonin da suke sauya sheƙ zuwa jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad, ya ce yana nan a jamiyyarsa ta PDP daram.

Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan jita-jitar da ake yaɗawa cewa yana shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

Gwamnan ya musanta hakan ne a wata hira da BBC ta yi da shugaban jam’iyyarsa ta PDP a jihar Bauchi wanda ya yi magana da yawun gwamnan.

Pharmacist Sama’ila Adamu Burga, shugaban jam’iyyar PDP a jihar Bauchi, ya ce jita-jita ce kawai.

“Da wa aka yi? kuma da wa gwamnan na Bauchi ya yi shawarar sauya shekar? to duk wannan jita-jitace kawai da soki burutsu,” in ji shi.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya