Abin da Bala Kaura ya ce kan rade-radin sauya shekarsa zuwa APC

Yayin da ake ci gaba da lissafa gwamnonin da suke sauya sheƙ zuwa jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad, ya ce yana nan a jamiyyarsa ta PDP daram.

Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan jita-jitar da ake yaɗawa cewa yana shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

Gwamnan ya musanta hakan ne a wata hira da BBC ta yi da shugaban jam’iyyarsa ta PDP a jihar Bauchi wanda ya yi magana da yawun gwamnan.

Pharmacist Sama’ila Adamu Burga, shugaban jam’iyyar PDP a jihar Bauchi, ya ce jita-jita ce kawai.

“Da wa aka yi? kuma da wa gwamnan na Bauchi ya yi shawarar sauya shekar? to duk wannan jita-jitace kawai da soki burutsu,” in ji shi.

Post masu alaƙa

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 26 a Borno

Tinubu ya tafi hutun mako uku

Gwamnatin Kwara ta haɗa mutum 146 da aka sace a Woro da iyalansu