Ƙusoshin adawa a Najeriya sun bayyana tsohon shugaban Majalisar Dattijan ƙasar David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), wadda suka amince da ita a matsayin jam’iyyar haɗaka.
Ƴan adawar sun ɗauki wannan mataki ne a taron da suka gudanarwa a Abuja, babban birnin Najeriya.
A jerin tattaunawar da suka gudanar na baya-bayan nan manyan masu adawa da gwamnatin ƙasar sun amince da ADC a matsayin jam’iyyar da za su yi amfani da ita domin ƙalubalantar shugaban ƙasar Bola Tinubu a babban zaɓe na shekarar 2027.
A wajen taron na yau Laraba an samu halartar manyan ƴan adawa da suka hada da Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El-Rufa’i da sauran su.