Home » An Wayi Gari Da Matsanancin Hazo A Kano

An Wayi Gari Da Matsanancin Hazo A Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

An wayi gari da hazo a sassan jihar Kano a safiyar Lahadi, inda ba a iya hango wanda ke sama da mita 500. 

A irin wannan yanayi, fitowa wuraren aiki kan yi wa mutanen da basu da mota wahala sakamakon sanyi da iskar da ke kaɗawa.

Ana sa ran za a cigaba da samun irin wannan yanayi har zuwa ƙarshen watan ɗaya zuwa farkon watan biyu na shekarar 2025 kamar yadda aka saba.

A irin wannan yanayi, masu cutar sarƙewar numfashi na fuskantar barazana, sakamakon yanayin bai dace da buƙatar lafiyarsu ba.

Hakan ta sa, ma’aikatan lafiya ke shawartar jama’a su riƙa kula da lafiyar su domin kaucewa hatsarin da ke tattare da ƙurar da ke tashi.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?