Mujahid Wada Guringawa

Gobara ta ƙone ajujuwa da ɗakin taro a GSSS Jalingo

Gobara ta ƙone ajujuwa da ɗakunan ajiya da kuma babban ɗakin taro a Makarantar Sakandaren Kimiyya ta Gwamnati (GSS) da ke Jalingo, a Jihar Taraba. Gobarar ta lalata kusan dukkan ajujuwan makarantar da littattafan karatu, da babban ɗakin jarabawa, lamarin da ya kawo cikas ga harkokin karatu a makarantar. Ana zargin gobarar ta fara ne […]

Read more

Magoya bayan Kwankwaso sun ƙi halartar taron Gwamna Abba

A daidai lokacin da raɗe-raɗen sauya sheƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf daga jam’iyyar NNPP zuwa APC ke ci gaba da ɗaukar hankali a Kano, an sake ganin wata sabuwar ɓarakar da ke nuna akwai tsamin dangantaka tsakanin gwamnan da jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso. A ƙarshen mako, wasu manyan magoya bayan Kwankwaso sun ƙaurace […]

Read more

An jibge motocin yaƙi a Gidan Gwamnatin Kano

An tsaurara ƙarin jami’an tsaro a gidan Gwamnatin Jihar Kano a safiyar Litinin a yayin da ake dakon sauya sheƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf. Wakilinmu ya lura cewa an girke ƙarin ’yan sanda da jami’an hukumar tsaro ta DSS a babbar ƙofar shiga da wasu muhimman wurare a gidan gwamnatin. Sojoji sun ceto fasinjojin da […]

Read more

Tinubu ya isa Abu Dhabi don halartar taron makamashi

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa domin halartar wani taron makon makamashi. Cikin wata sanarwar da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta ce Shugaba Tinubu ya samu tarba daga ministan harkokin wajen ƙasar UAE, Sheikh Shakhboot Nahyan Al Nahyan, da jakadan UAE a Najeriya a ƙasar, Salem […]

Read more

Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin ƙarfafa dakarun ƙasar

Gwamnatin Najeriya ta alƙawarta sake ƙarfafa dakarun tsaron ƙasar domin magance matsalar tsaro da ke addabar wasu sassan ƙasar. Mataimakin Shugaban Ƙasar, Kashim Shettima ne ya bayyana haka a lokacin taron addu’o’i na musamman ga dakarun tsaron ƙasar da aka gudanar a Babban Masallacin Juma’a na ƙasa da ke Abuja, babban birnin ƙasar. Shettima ya […]

Read more