Labarai

Babban Labari Labarai

Yan Sanda Sun Kama Matar Da Ake Zargi Da Koyawa Matasa Laifuka A Jigawa.

Rundunar yan sandan jihar Jigawa, ta samu nasarar kama wata matashiya, mai suna Shamsiyya Muhammad yar shekaru 28 mazauniyar Gidan Ruwa, bisa zarginta da koyawa matasa maza da mata hanyoyin aikata laifuka. Kakakin rundunar yan sandan jihar Jigawa, SP Shiisu Lawan Adamu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da aikewa da manema labarai. […]

Babban Labari Labarai

Rikicin Cikin Gida Ya Turnuƙe APC A Kano

Wata sabuwar dambarwa ta sake tasowa a cikin gidan jam’iyyar APC a jihar Kano, kwanaki kaɗan bayan saukar Abdullahi Umar Ganduje daga shugabancin APC na ƙasa. Wasu ƴaƴan jam’iyyar sun fito suna neman shugaban APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas wanda na hannun daman Ganduje ne, ya sauka daga muƙaminsa, lamarin da ɓangaren Abdullahi Abbas […]

Babban Labari Labarai

Horon Da Muka Samu A Kasar Amurika Zai Yi Tasiri Wajen Magance Fadan Daba: SP Abdullahi H Kiyawa

  Rundunar yan sandan Nijeriya reshen jihar Kano, ta lashi takobin ci gaba da yaki da masu kwacen waya da harkar daba da sauran miyagun laifuka a fadin jihar. Kakakin rundunar yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan kwanaki kadan bayan daworsa daga wani taro na musamman da ya halatta, […]

Babban Labari Labarai

An Kammala Dawo Da Alhazan Nijeriya.

Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta sanar da kammala dawo da dukkan  alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana gida Najeriya daga kasar Saudiyya. A cikin wata sanarwar da Daraktar Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Laraba, ta ce jirgin karshe dauke da alhazai 88 ya bar birnin […]

Babban Labari Labarai

An Naɗa David Mark A Matsayin Shugaban Jam’iyyar ADC

Ƙusoshin adawa a Najeriya sun bayyana tsohon shugaban Majalisar Dattijan ƙasar David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), wadda suka amince da ita a matsayin jam’iyyar haɗaka. Ƴan adawar sun ɗauki wannan mataki ne a taron da suka gudanarwa a Abuja, babban birnin Najeriya. A jerin tattaunawar da suka gudanar na baya-bayan […]

Babban Labari Labarai

Tsohon Ministan Shari’ar Nijeriya Abubakar Malami Ya Koma Jam’iyar ADC

Tsohon ministan shari’a na Najeriya, Abubakar Malami ya sanar da ficewa daga jam’iyyar APC tare da komawa haɗakar ƙawancen jam’iyyu hamayya ta ADC. Cikin wata sanarwa da tsohon ministan ya fitar a shafinsa na sada zumunta, ya ce ya ɗauki matakin ne domin bayar da tasa gudunmowa wajen ceto Najeriya daga durƙushewa. Abubakar Malami ya […]

Babban Labari Labarai

An Gudanar Da Jana’izar Alhaji Aminu Ɗantata A Birnin Madina

An gudanar da jana’izar hamshaƙin ɗankasuwar nan na Najeriya, Marigayi Alhaji Aminu Ɗantata a masallacin Annabi (S.A.W) da ke birnin Madina. Jana’izar ta gudana ne bayan sallar magariba, inda kuma aka binne gawarsa a maƙabarta Baƙiyya mai tarihi a birnin na Madina. Mutane da dama ne daga Najeriya suka halarci jana’izar – wadda aka jinkirta […]

Babban Labari Labarai

Gwamnan Bauchi Zai Kirƙiro Sabbin Masarautu

Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi ya amince da kafa kwamitin mambobi 41 da nufin kafa sabbin masarautu a faɗin jihar. Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar ta bayyana cewa kwamitin ya ƙunshi fitattun mambobi 41 da aka zabo daga ɓangarori daban-daban, ciki har da sarakunan gargajiya, ƙwararru, malaman jami’a, wakilan ƙungiyoyin […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000