Yan Sanda Sun Kama Matar Da Ake Zargi Da Koyawa Matasa Laifuka A Jigawa.
Rundunar yan sandan jihar Jigawa, ta samu nasarar kama wata matashiya, mai suna Shamsiyya Muhammad yar shekaru 28 mazauniyar Gidan Ruwa, bisa zarginta da koyawa matasa maza da mata hanyoyin aikata laifuka. Kakakin rundunar yan sandan jihar Jigawa, SP Shiisu Lawan Adamu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da aikewa da manema labarai. […]










