Labarai

Babban Labari

Zaɓen cike gurbi: Rundunar ƴan Sandan jihar Kano ta taƙaita zirga-zirga a Dawakin Kudu da Warawa.

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta bayyana matakan tsaro da aka amince da su gabanin zaben cike gurbin ɗan majalisar Tarayya mai wakiltar Dawakin Kudu da Warawa wanda zai gudana ranar Asabar. Wannan na ƙunshe cikin wata sanarwa da kakakin rundunar,CSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar Yace bisa umarnin kwamishinan yan sandan jihar Kano,  CP […]

Babban Labari

DIG Sulaiman M Abdul ya gana da masu ruwa da tsaki kan tsaro a Kano.

Babban sufeton ƴan sandan Nijeriya, Olatunji Rilwan Disu, ya yabawa dakarun rundunar ƴan sandan jihar Kano, bisa nasarorin da suka samu wajen yaƙi da masu aikata laifuka da murƙushe yunƙurin kutsowar ƴan bindiga tare da tabbatar da zaman lafiya a jihar. Olatunji Disu, wanda ya samu wakilcin muƙaddashin sufeton ƴan sandan Najeriya, DIG Sulaiman Muhammed […]

Babban Labari Babu Rukuni

Rundunar ƴan sandan Nijeriya ta kafa kwamitin da zai nemo hanyoyin da jami’anta za su mallaki gidaje.

Rundunar ƴan sandan Nijeriya ta ƙirƙiro wani kwamiti da zai  fito da hanyoyin da kowanne jami’in ɗan sanda zai mallaki muhalli ba tare da yasha wahala ba. Muƙaddashin babban sufeton ƴan sanda Najeriya, DIG Sulaiman Muhammed Abdul, ne ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da dakarun ƴan sandan jihar Kano, a madadin shugaban ƴan […]

Babban Labari

Kotu ta umurci INEC ta soke rijistar jam’iyyar ADC

Wata babbar Kotun Tarayyar Najeriya ta umurci hukumar zaɓen ƙasar INEC ta soke rajistar jam’iyyar adawa ta ADC da wasu jam’iyyu huɗu. Kotun da ke Abuja ta ce jam’iyyun sun gaza cika sharuɗan da kundin tsarin mulkin kafa jam’iyyun siyasa. Mai Shari’a Peter Lifu ne ya yanke hukuncin, inda ya ce jam’iyyun ba su samu […]

Babban Labari

Ɗan Kwankwaso ya zama ɗan takarar Mataimakin Gwamnan Kano a NDC

Ɗan takarar gwamnan Jihar Kano a jam’iyyar NDC, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya zaɓi Mustapha Rabiu Musa Kwankwaso, ɗan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a matsayin abokin takararsa na mataimakin gwamna a Zaɓen 2027. Mustapha Kwankwaso, wanda tsohon Kwamishinan Matasa da Wasanni ne a gwamnatin Abba Kabir Yusuf, ya yi murabus daga muƙaminsa, inda ya koma tafiyar […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai