Labarai

Babban Labari

Dan Sarkin Daura ya fito takarar dan Majalisar Wakilai

Muhammad Daha, ɗa ga Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Majalisar Tarayya mai wakiltar Baure/Zango a zaɓen 2027. Daha, wanda ke rike da sarautar Danburam na Daura, ya ce matakin ya biyo bayan kiraye-kiraye  daga al’ummarsa da ke son ya wakilce su a Majalisar Tarayya. “Ina […]

Babban Labari

Majalisar dokokin Kano ta jingine tuhumar da take wa tsohon mataimakin gwamna Aminu Abdussalam

Majalisar dokokin jihar Kano tace ta janye tuhume tuhumen da take yiwa tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, biyo bayan ajiye mukamin sa na Mataimakin Gwamna Jahar Kano Majalisar ta bayyana hakan ne a zaman ta na yau karkashin Jagorancin Rt Hon Jibrin Isma’il Falgore. Da yake ƙarin haske dangane da lamarin, […]

Babban Labari

Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi ya rasu.

Allah Ya yi wa Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Muhammad Usman Zuru, rasuwa a wani asibiti da ke ƙasar Masar, inda yake karɓar magani sakamakon fama da dogon rashin lafiya da ba a bayyana ba. Wani jami’in gwamnati a Birnin Kebbi ya ce an kai shi kasar waje domin jinya tun kafin fara azumin watan Ramadan […]

Babban Labari

Harsashi daga wurin biki ya yi ajalin wata budurwa mai shekaru 14 a Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Wata budurwa ‘yar shekara 14 ta rasa rayuwata bayan wani harsashi da ake kyautata zaton an harbo shi daga wurin bikin aure a tsallako gidansu da ke rukunin gidajen ma’aikatan Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri a ranar Asabar. Da farko dai an ce bikin na sojoji ne, amma daga bisani babban kwamandan rundunar Operation Haɗin […]

Babban Labari

Gwamnonin Arewa sun yi alhinin rasuwar matar Farfesa Jega

Gwamnonin jihohi 19 na Arewacin Najeriya sun miƙa ta’aziyyarsu ga tsohon Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, bisa rasuwar matarsa, Hajiya Hadiza. Hajiya Hadiza ta rasu ne a ranar Lahadi, kuma an yi jana’izarta bisa koyarwar addinin Musulunci bayan gudanar da sallar jana’iza a Masallacin Ƙasa da ke Abuja. Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin […]

Babban Labari

Ƙaramar ministar ƙwadagon Najeriya ta yi murabus

Ƙaramar Ministar kwadagon Najeriya Nkeiruka Onyejeocha ta yi murabus daga muƙaminta. Ta sanar da murabus ɗin nata ne a shafinta na X, inda ta miƙa godiyarta ga shugaba Bola Ahmed Tinubu wanda ya bata dama ta yi aiki da gwamnatinsa. Ta bayyana ajiye muƙamin nata a matsayin matakin rufe wani gagarumin babi na rayuwarta a […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai