Labarai

Babban Labari

Gobara ta yi ajalin ɗalibai 16 a Kenya

Ɗalibai 16 sun mutu sakamakon wata gobara da ta tashi a makarantar kwana da ke Gilgil a Kenya, kamar yadda wani ɗansanda ya shaida wa manema labarai. Wasu ɗalibai 74 kuma suna samun kulawa a asibiti bayan raunin da suka ji. Gobarar da ta faru a makarantar ƴanmata ta Utumishi ta soma ne da sanyin […]

Babban Labari

Sanata Omo-Agege ya fice daga APC

Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Ovie Omo-Agege ya fice daga Jam’iyyar APC mai mulki. Cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara ka harkar labarai, Sunday Areh ya fitar, Sanata Omo-Agege ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓa da ya yi da makusantansa a siyasa da kuma magoya bayansa, bugu da ƙari […]

Babban Labari

Kwamishinan ƴan sandan Kano CP Ibrahim Adamu Bakori ya gargaɗi masu yunƙurin tayar da hankalin jama’a lokacin bikin sallah

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta bayyana cewa ba zata lamunci duk wani yunƙuri na tayar da hankalin jama’a, ko yin abun da zai kawo cikas ga tsaro da zaman lafiya, yayin gudanar da bikin babbar Sallah na shekarar 2026 ba. Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana hakan ta […]

Babban Labari

Rundunar ƴan sandan Nijeriya shiya ta ɗaya ta tsaurara tsaro gabanin Babbar Sallah

Rundunar ƴan sandan Nijeriya shiya ta ɗaya dake jihar Kano, ta bayyana cewa ta ɗauki tsauraran matakan tsaro, kamar yadda babban sufeton ƴan sadan Nijeriya, IGP Olatunji Rilwan Disu, ya bayar da umarni, don tabbatar da an gudanar da bukukuwan babbar sallah cikin kwanciyar hankali da lumana. Mataimakin sufeton ƴan sandan Nijeriya shiya ta ɗaya, […]

Babban Labari

An kama mutum 4 kan damfarar maniyyata a Kebbi

Wasu mutum huɗu da ake zargi da damfarar maniyyata aikin Hajjin bana sun shiga hannu a Jihar Kebbi. Jami’in hulɗa da jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta, SP Bashir Usman, ya bayyana cewa dubun waɗanda ake zargin ta cika ne bayan ƙorafe-ƙorafe daga waɗanda abin ya shafa da kuma Hukumar Jin Daɗin Alhazai […]

Babban Labari

Hukumar Road Safety Za Ta Ɗauki Tsattsauran Matakai Kan Masu Tuƙin Ganganci A Kano.

Hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa reshen jihar Kano, ta ƙudirin aniyar ɗaukan tsattsauran mataki ga duk wanda aka kama da laifin yin tuƙin ganganci a lokutan bukukuwan babbar sallah. Jami’in hulɗa da jama’a da wayar da kai na hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa reshen jihar Kano, CRC Abdullahi Labaran, ne ya bayyana hakan yayin tattaunawarsa […]

Babban Labari

Majalissar dinkin duniya ta ce miliyoyin mutane a Najeriya na iya fuskantar matsananciyar yunwa

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa miliyoyin ’yan Najeriya na iya fuskantar matsananciyar yunwa a watanni masu zuwa sakamakon matsalar tsaro, rikice-rikice da kuma tsadar rayuwa da ke ƙaruwa a faɗin ƙasar. Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya (OCHA), ta ce iyalai da dama za su shiga wani yanayi da ka […]

Babban Labari

Ebola: An dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a Congo

Hukumomi a Jamhuriyar Dimokraiyyar Kongo sun dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa yankin Bunia babban binin Ituri har illa masha Allahu, saboda barazanar yaduwar cutar Ebola. Sanarwa daga ma’aikatar sufurin ƙasar ta nuna cewa za a tantance jiragen kayan jin ƙai, da na ma’aikatan lafiya, kuma za a bukaci izini daga hukumomin lafiya da na […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai