Labarai

Ko Makiyan Buhari Sun San Bai Yi Sata Ba: Akpabio

Shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio, ya kwatanta marigayi shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a matsayin shugaba na gari wanda ya mulki Najeriya ba tare da satar duƙiyar ƙasa ba. Akpabio, wanda ya bayyana haka a lokacin taron majalisar zartaswa da aka gudanar a Abuja don yi wa tsohon shugaban addu’o’i, ya ce masu sukarsa ma […]

Read more

Tinubu Ya sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Muhammadu Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari, marigayi shugaban Najeriya. Tinubu ya sanar da haka ne a taron majalisar zartaswa da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja. “Kafin mu fara addu’o’i domin karrama Buhari, ina sanar da ku cewa mun sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari,” in […]

Read more

Tinubu Zai Jagoranci Taron Yi Wa Buhari Addu’o’i A Abuja

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai jagoranci taron addu’o’i na musamman ga tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari a Abuja, babban birnin ƙasar. Cikin wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labaran ƙasar ta fitar ta ce taron – wanda za a gudanar da misalin ƙarfe biyar na maraice agogon ƙasar – zai samu halartar ministocin gwamnatin ƙasar. Bayan […]

Read more

Dele Momodu Ya Fice Daga PDP

Fitaccen ɗan siyasa kuma tsohon gogaggen ɗanjaridar nan na Najeriya, Dele Momodu ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar PDP zuwa sabuwar haɗakar ADC ta an hamayya. Domodu – wanda ya taɓa tsayawa takarar shugaban ƙasar – ya ce ya ɗauki matakin ne saboda yadda wasu da ya kira ”masu yaƙi da dimokraɗiyya” suka hana jam’iyyar numfashi. […]

Read more

Dangote Zai Gina Tashar Jiragen Ruwa Mafi Girma

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya mika takardun neman izinin gina tashar jiragen ruwa mafi girma da zurfi a fadin Najeriya a jihar Ogun. Da yake tattaunawa da jaridar Bloomberg ta Birtaniya, attajirin na Afrika ya ce tuni ya aike da bukatar tasa domin fara aiki a gabar ruwa ta Olokola da ke […]

Read more

An Binne Gawar Marigayi Muhammadu Buhari A Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura na jihar Katsina da misalin karfe 5:50 na yamma. A ranar Lahadi, 13 ga watan Yuli ne Muhammadu Buhari ya rasu a birnin Landan na Birtaniya bayan shafe dogon lokaci yana jinya. Muhammadu Buhari ya rasu ne yana da shekara 82 a […]

Read more