Abuja: An Fara Rufe Hanyoyi Domin Tabbatar da Tsaro a Ranar Rantsar da Sabon Shugaban Ƙasa
Hukumomi a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya, sun ba da izinin rufe wasu hanyoyi da suka dangana da gine-ginen Sakatariyar Gwamnatin Tarayya da Ma’aikatar Harkokin Wajen kasar saboda faretin rantsar da sabuwar gwamnati da za a yi.