INEC Ta Ayyana Zaɓen Jihar Adamawa a Matsayin Wanda Bai Kammala Ba

Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta ayyana zaben gwamnan jihar Adamawa a matsayin wanda bai kammala ba, watau “Inconclusive.”

Jami’in hukumar ta INEC wanda ke da alhakin tattara sakamakon zabe a jihar ya ce adadin katin zabe na dindindin da mutane suka karba a yankunan da aka samu matsala 37,000 ya zarce tazarar da ke tsakani.

A cewarsa, adadin ya zarce tazarar da ke tsakanin gwamna Ahmadu Fintiri na PDP da babbar abokiyar karawarsa, Sanata Aishatu Binani, ta jam’iyyar APC, kamar yadda majiyarmu ta rawaito.

Post masu alaƙa

Ƙungiyoyin PDP 293 sun koma APC a Yobe

An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen cike gurbi a Kano

APC ta fara faɗawa tarkon rikici a jihar Kano