DSS Ta Kori Wasu Jami’anta 115 Daga Aiki

Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya, DSS ta ce ta kori wasu jami’anta 115 daga aiki, saboda abin da ta kira wasu sauye-sauye da hukumar ke yi.

Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, a ranar Talata, DSS ta shawarci al’umma su kauce wa mu’amala da jami’an a matsayin wakilan hukumar.

Hukumar ta kuma wallafa sunaye da hotonan jami’an 115 da ta ce ta koran a shafinta intanet.

Bayanan mutanen da hukumar ta fitar sun nuna cewa an kori mutanen ne tsakanin shekarar 2024 zuwa 2025.

Matakin na zuwa ne bayan da a watan Oktoban da ya gabata hukumar ta kama wasu tsoffin jami’anta biyu bisa zargin amfani sa sunan hukumar suna damfarar mutane.

Post masu alaƙa

Katsina ta kafa kotunan tafi da gidan ka don gaggauta hukunta ’yan ta’adda

‘Talauci ya faɗo daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun