Home » Gwamnan Jigawa Ya Jaddada Aniyarsa Ta Inganta Neman Ilimin Alqur’ani A Jihar 

Gwamnan Jigawa Ya Jaddada Aniyarsa Ta Inganta Neman Ilimin Alqur’ani A Jihar 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da inganta tsarin koyar da Alkur’ani a jihar, ya yi kafaɗa da kafaɗa da tsarin neman ilimi a zamani. 

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin rufe gasar karatun Alkur’ani ta jihar karo na 40, da aka gudanar a Dakin Taro na Sir Ahmadu Bello da ke Dutse.

Ya bayyana matasan da ke haddace Alkur’ani a jihar a matsayin “babbar ni’ima” ga al’umma, inda ya yi nuni da muhimmancin ilimin Alkur’ani wajen gyara hali da saukaka rayuwa.

Gwamna Umar Namadi ya buƙaci mahalarta gasar da su yi rayuwa da koyarwar Alkur’ani.

“Kasancewar waɗannan matasa da suka haddace Alkur’ani a cikinmu babbar ni’ima ce. Muna ganin amfanin wannan gasa ta karatun Alkur’ani da ake gudanarwa. Idan mutum ya samu ilimin addini, musamman na Alkur’ani, komai na rayuwa zai zo masa sauki,” in ji shi.

“Saboda haka, muna gode wa Allah da wannan rahama da Ya yi mana na bamu matasa masu baiwar haddace Alkur’ani.”

Ya kara da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafawa ilimin Alkur’ani ta hanyar Hukumar Tsangaya, wacce aka kafa domin hada ilimin Alkur’ani da tsarin karatun zamani da yi masa kasafin kudi na musamman.

Haka kuma, ya bayyana cewa za a tallafa wa daliban da suka fi kwarewa domin ci gaba da karatunsu, ko dai a bangaren ilimin addini ko kuma fannin zamani kamar injiniyanci da likitanci.

Ya yaba wa Hukumar Ilimin Addinin Musulunci ta Jihar Jigawa, Hukumar Tsangaya, da Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi saboda kokarin da suke yi wajen bunkasa ilimin Alkur’ani.

A bana (2025), gasar ta kunshi maza da mata a fannoni daban-daban da suka hada da karatun hizibi biyu, goma, talatin da kuma sittin na Alkur’ani mai girma.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?