Gwamnan Osun Ya Buƙaci Tattaunawa Tsakanin Najeriya Da Amurka

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya yi kiran sabunta tattaunawar diplomasiyya tsakanin Najeriya da Amurka, yayin da ake samun ƙaruwar nuna yatsa tsakanin ƙasashen biyu.

Cikin wata sanarwa da kakain gwamnan, Olawale Rasheed ya fita,, Gwamnan Adeleke ya buƙaci a tattauna kan barazanar da Shugaban Amurka ya yi a baya-bayan nan kan kai wa Najeriya hari.

Trump ya yi barazanar kai wa Najeriya hare-hare sakamakon abin da ya kira yawan kisan kiristoci a ƙasar.

Gwamnan ya yi kira a samar da wata hanyar lalama domin samo bakin zaren tsakanin ƙasashen biyu.

“Ina kira ga fadar shugaban Amurka ta tallafa wa Najeriya wajen aiwatar da sabbin dabarun tsaro na zamani”, in ji shi.

Post masu alaƙa

Fursuna ya tsere bayan hatsarin motar jami’ai a Yobe

Katsina ta kafa kotunan tafi da gidan ka don gaggauta hukunta ’yan ta’adda

‘Talauci ya faɗo daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto