Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan 99 domin rigakafin cutar mahaukacin kare

Gwamnatin jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan 99 domin fara shirin rigakafin cutar mahaukacin kare (rabies), inda ake sa ran yi wa akalla karnuka 10,000 allurar rigakafi a mataki na farko.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktar Wayar da Kai ta Ma’aikatar Raya Dabbobi ta jihar, Halima Gadanya, ta fitar a ranar Asabar.

Sanarwar ta ce gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ne ya bayar da amincewar a matsayin wani bangare na kokarin gwamnatinsa na kare lafiyar al’umma daga cututtukan da ake iya kauce musu amma masu hadari.

Shirin zai kasance karkashin jagorancin Ma’aikatar Raya Dabbobi ta jihar, inda kwamishinan ma’aikatar, Aliyu Isah Aliyu, zai kula da aiwatar da shi kamar yadda jaridar Punch ta ambato.

 

Post masu alaƙa

Yan sanda sun kama mutane 79 tare da kwato kwayoyi da makamai a bikin Takutaha a Kano.

Yan sanda sun kama wanda ake zargi da damfarar masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 40.

Sabuwar majalisar gudanarwa ta POLAC za ta mayar da hankali kan inganta da ilimi da horo.