Hisbah A Jihar Katsina Ta Lalata Barasar Naira Miliyan 60

HISBAH KATSINA

Dakarun Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, sun lalata barasa da ƙwayoyi da ta ƙwace da kuɗinsu ya kai kimanin Naira miliyan 60 a Ƙaramar Hukumar Funtua da ke jihar Katsina.

Dokta Aminu Usman Kwamandan Hisbah na jihar Katsina ne ya sanar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN).

Dokta Aminu ya ce, hukumar ta ƙwace  giya kwalaye 1,750 da jarkoki 33 da aka sarrafa su a cikin Funtua.

Kwamandan ya jinjina wa ma’aikatan hukumar kan ƙoƙarinsu, ya kuma buƙaci su matsa kaimi wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Kwamandan na Hisbah a jihar Katsinaa ya roƙi shugabannin Addini a jihar da su tallafa wa hukumar, inda ya ce Hisbah ta kowa ce ba ta da gefe.

Post masu alaƙa

Alarammomi sun amince da tsarin haɗa ilimin boko da na addini a Jigawa

Gwamnati za ta mayar da yara 5,000 makaranta a Jigawa

Ba mu ƙarƙare batun sauya kayan NYSC ba – Ministan Matasa