Hukumar Ƙirƙira Ta Ƙasa Ta Ziyarci KILAF

Ƙungiyar Shirya Fina-finanai a Harsunan Nahiyar Afirika ta KILAF ta karɓi baƙuncin Hukumar Ƙirƙirar Da Fasaha Ta Najeriya (National Gallery of Arts) domin ƙara ƙarfafa alaƙar da take tsakani. 

Tattaunawar su ta mayar da hankali ne wajen taron da KILAF ɗin za ta shirya a ranar 25 zuwa 30 ga watan Nuwamban shekarar, 2024.

Ana sa ran taron zai gudana ne a babban ɗakin taro na Ado Bayero dake Kano, inda za’a baje kolin kayayyaki da kuma shirye-shiryen da suka shafi al’adu.

Bakin sun samu tarba ta musamman daga babban daraktan KILAF Alhaji Abdulkareem Muhammad

Post masu alaƙa

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.