Kasar Sin da Amurka Sun Amince da Kawo Karshen Zaman Doya da Manja da Suke Yi

Ƙasar China da Amurka sun yi tsokaci kan ci gaban da aka samu wajen amincewa su ci gaba da hulɗa a tsakaninsu bayan kwashe wasu lokuta suna zaman doya da manja.

Wata sanarwa da aka fitar bayan taron da manyan jami’an diplomasiyyar ƙasashen suka yi a China, ta bayyana cewa an samu ci gaba sosai a tattaunawar da ƙasashen biyu suka yi.

Daga cikin batutuwan da sanarwar mai ɗauke da sa hannun mataimakin sakataren ƙungiyar ƙasashen gabashin Asiya da na yankin pacific, ta fitar, har da batun ‘yancin ɗan adam da kuma halin da ake ciki a Taiwan.

Ya ce Amurka na kokari sosai wajen daidaita dangantakarta da China.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Kotu tsare mutane biyu da ake zargi da rushe Gadar Watari da yanka filaye ba bisa ka’ida ba a Kano.

Rundunar yan sandan Kano ta kwato motar da aka sace sannan aka siyar da ita a Nijar