Majalisa Za Ta Binciki Zargin Rashin Ingancin Matatar Man Dangote

Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abbas ya ce za a gudanar da bincike kan zargin da ake yi cewa man fetur ɗin da ake samu daga matatar Dangote bai kai kyau da ingancin wanda ake shigowa da shi daga ƙasashen ƙetare ba.

Tajudeen Abbas ya sanar da hakan ne a ziyarar da ƴan majalisar suka kai matatar man ta Dangote a ranar Asabar.

Abbas ya bayyana damuwarsa kan cece-ku-cen da ake tafkawa dangane da ingancin man da ake shigowa da shi Najeriya.

Alhaji Aliko Dangote, ya tabbatar da cewa kayan sarrafa man fetur da matatarsa ke amfani da su ingantattu ne kuma sun cika duk wata ƙa’idar Najeriya da ma ta ƙasa da ƙasa.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun ceto mutum 31 da aka sace a Zamfara

Gwamnonin Najeriya na duba yiwuwar mayar da mafi karancin albashi N100,000

Rundunar ƴan sandan Kano ta yaba da zaman lafiyar da aka samu lokacin bikin babbar sallah