Malam El-Rufa’i Ya Koma Jamiyyar SDP

Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufa’i ya tabbatar da sauya sheƙa daga jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar zuwa jam’iyyar SDP.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ya wallafa ranar Litinin ne a shafukansa na sada zumunta.

El-Rufai ya ce, “yanzu na yanke shawarar komawa jam’iyyar Social Democratic Party, kuma zan kasance a cikin ta wajen tafiyar da al’amurana na siyasa a nan gaba.

Kwanakin baya a lokacin tattaunawarsa da kafar talabijin ta Arise, El-Rufa’i ya bayyana cewa “jam’iyyar APC ta sauka daga kan manufofin da aka assasa ta tun fil-azal.”

Ya yi zargin cewa jam’iyyar ta gaza kiran taron shugabanninta na ƙasa tsawon shekaru, wanda ya ce hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

A yanzu dai wannan ya kawo ƙarshen raɗe-raɗin da ake yi na inda tsohon gwamnan zai nufa bayan raba gari da jam’iyyar APC.

Post masu alaƙa

Rukunin farko na ‘yan Najeriya da aka kwashe daga Afirka ta Kudu zai isa ƙasar ranar Alhamis

Gwamnatin Sakkwato ta tallafa wa Alhazai 47 da suka ɓatar da kuɗin guzurinsu

An kammala shirye-shiryen tabbatar da tsaro a zaɓen cike gurbin ɗan majalissar wakilan Dawakin Kudu/Warawa a Kano.