Sojoji Sun Halaka Ƴan Ta’adda 80 A Katsina

Jirgin Sojin Najeriya mai saukar Ungulu

Rundunar sojojin saman Najeriya ta ce ta halaka sama da ƴan ta’adda 80, a wani ƙauyen jihar Katsina. 

Ta ce ta yi nasarar ƙone baburansu 45 sakamakon luguden wutar da ta yi musu a daren ranar Asabar ɗin da ta gabata.

Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da rundunar sojin sama ta Najeriya ta fitar a ranar Litinin.

Sanarwar da daraktan hulɗa da jama’a da yaɗa labarun rundunar sojin, Edward Gabkwet ya sanyawa hannu, ta ce an kai harin ne a wata maɓoyar ƴan bindigar da ke ƙauyen Gidan Kare a ƙaramar hukumar Faskari.

Sanarwa sojojin ta ce ta kai harin ne a daren ranar Asabar a lokacin da ta samu rahoton cewa ƴan ta’adda kimanin 100 sun kai hari a wani ƙauyen da ke da nisan kilomita biyar daga Gidan Kare, inda suka ƙone gidajen jama’a.

Post masu alaƙa

Gwamnati ta buƙaci jama’a su guji taɓa kumfar da ta ɓulla a hanyar Kaduna-Abuja

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China