Sojoji Sun Halaka Ƴan Ta’adda 80 A Katsina

Jirgin Sojin Najeriya mai saukar Ungulu

Rundunar sojojin saman Najeriya ta ce ta halaka sama da ƴan ta’adda 80, a wani ƙauyen jihar Katsina. 

Ta ce ta yi nasarar ƙone baburansu 45 sakamakon luguden wutar da ta yi musu a daren ranar Asabar ɗin da ta gabata.

Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da rundunar sojin sama ta Najeriya ta fitar a ranar Litinin.

Sanarwar da daraktan hulɗa da jama’a da yaɗa labarun rundunar sojin, Edward Gabkwet ya sanyawa hannu, ta ce an kai harin ne a wata maɓoyar ƴan bindigar da ke ƙauyen Gidan Kare a ƙaramar hukumar Faskari.

Sanarwa sojojin ta ce ta kai harin ne a daren ranar Asabar a lokacin da ta samu rahoton cewa ƴan ta’adda kimanin 100 sun kai hari a wani ƙauyen da ke da nisan kilomita biyar daga Gidan Kare, inda suka ƙone gidajen jama’a.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM