Son Zuciya Da Rashin Kishi Ke Kai ‘Yan Arewa APC -Tambuwal
Tsohon Gwamnan Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, ya bayyana cewa guguwar sauyin sheƙa da ke kaɗawa a tsakanin jam’iyyun siyasa a Arewa maso Yammacin ƙasar na da alaƙa da son zuciyar ’yan siyasar yankin.








