Tag: jigawa

Babban Labari Labarai

Kamfanin Maltina yasha alwashin samarwa mutane 20,000 aiki nan da shekarar 2030 a Nijeriya.

Kamfanin Maltina ya bayyana cewa zai samar da ayyukan yi ga manoma sama da 20,000 a jihar Jigawa nan da shekarar 2030, a wani sabon shiri da kamfanin ya ƙaddamar domin bunƙasa noman sha’ir (Maltina Barley Field Day) da kuma ƙarfafa tattalin arzikin al’umma. Shirin, wanda aka ƙaddamar da nufin tallafa wa manoma su rungumi noman zamani, […]

Babban Labari Labarai

Gwamnan jihar Jigawa Mallam Umar Namadi Ya rage lokacin aikin ga ma’aikata Saboda azumi

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da rage lokutan aiki ga ma’aikatan gwamnati a lokacin azumin watan Ramadan. ‎ ‎Gidan Rediyon Jihar Jigawa ya rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Shugaban Ma’aikatan Jihar, Muhammad K Dagaceri, ya sanyawa hannu a ranar Laraba 18 ga Fabrairu 2026. ‎ ‎Sanarwar ta ce bisa sabon […]

Uncategorized

Jigawa Ta Dakatar da ‘Yan Kwangilar Ciyar da Ɗalibai Saboda Zargin Damfara da Rashin Ingancin Abinci

Daga Ali Rabiu Ali, Dutse Ma’aikatar Jin-ƙai da Ayyuka na Musamman ta Jihar Jigawa ta dakatar tare da sallamar wasu ‘yan kwangilar ciyar da ɗalibai a makarantun kwana, bisa zargin yin almundahana, ƙara adadin ɗalibai ba daidai ba, da kuma samar da abinci mara inganci. Matakin ya biyo bayan binciken bazata (sting operation) da ma’aikatar […]

Babban Labari Labarai

Majalissar zartarwar Jigawa ta amince da kwangiloli na sama da naira biliyan 91

Majalisar Zartarwar Jihar Jigawa ta amince da bayar da kwangiloli da darajarsu ta haura naira biliyan 91, domin aiwatar da manyan ayyukan raya kasa a sassa daban-daban na jihar. Kwamishinan Lafiya, Dakta Muhammad Abdullahi Kainuwa, ya bayyana cewa taron majalisar ya gudana ne karkashin jagorancin Gwamna Malam Umar Namadi, a ranar 17 ga Disamba, 2025, […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai