Tinubu Ya Buƙaci Sojoji Su Killace Dazukan Kwara, Kebbi Da Neja

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci, jami’an tsaron ƙasar su killace dazukan jihohin Kwara da Kebbi da kuma Neja, inda a baya-bayan nan ake samun ƙaruwar hare-hare tare da garkuwa da mutane.

Cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban ƙasar kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Daare ya wallafa a shafinsa na X, ya ce Tinubu ya buƙaci runsunar sojin saman ƙasar ta faɗaɗa sanya idanu ta sama kan dazukan, waɗanda ya yi imanin cewa nan ne mafakar yanbindigar.

Shugaba Tinubu ya buƙaci sojojin saman su faɗaɗa tsaron dazukan domin taimaka wa dakarun ƙasa.

A baya-bayan nan ne dai an samu garkuwa da ɗaliban a jihohin Kebbi da Neja da masu ibada a jihar Kwara

Post masu alaƙa

Kwankwaso ya amince a ba wa Kudu takarar Shugaban Kasa ta NDC

Yan sandan Kano sun shirya taron masu duwa da tsaki bayan zanga-zanga a Ungogo

Najeriya ta ƙarfafa ƙawancen tsaronta da Amurka