Home » Tinubu Ya Kammala Wa’adin Mulkinsa A ECOWAS 

Tinubu Ya Kammala Wa’adin Mulkinsa A ECOWAS 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Shugaba Tinubu ya miƙa ragamar shugabancin Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ga Shugaban Ƙasar Saliyo, Julius Maada Bio. 

Yanzu shugaba Saliyo, Julius Maada Bio ne zai cigaba da jagorancin Ƙungiyar ta ECOWAS.

Yayin jawabin kama aiki, sabon shugaban na ECOWAS ya ce, “Dole mu sake fasalin ECOWAS ta yadda za ta zama mai gaskiya, inganci da amsa buƙatun al’ummarta,”

Shugaba Tinubu ya yi fama da matsaloli da yawa yayin shugabancin ƙungiyar, inda a lokacin shugabancinsa ne ƙasar Nijar da Burkina Faso da Mali suka fice daga ƙungiyar.

An kafa ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka ne a ranar 28 ga watan Mayu a shekarar 1975.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?