Tinubu ya tura Badaru Neja saboda matsalar sace ɗalibai

Gwamnatin Najeriya ta tura babban ministan tsaron ƙasar, Muhammad Badaru Abubakar, zuwa jihar Neja inda aka sace ɗalibai ‘fiye da 200’.

Ƙaramin ministan tsaron ƙasar, Muhammed Bello Matawalle ne ya bayyana haka ranar Juma’a da maraice a cikin shirin Ra’ayi Riga na BBC Hausa.

”Shi ma Badaru zai je Neja kamar yadda aka turoni Kebbi, domin ƙoƙarin gwamnati na kuɓutar da ɗaliban da aka sace”, in ji shi

Tuni dai Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura ƙaramin ministan tsaron zuwa jihar Kebbi – inda ƴanbindiga suka sace ɗalibai ƴanmata 25 – domin sanya idanu kan ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban.

Post masu alaƙa

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 26 a Borno

Tinubu ya tafi hutun mako uku

Gwamnatin Kwara ta haɗa mutum 146 da aka sace a Woro da iyalansu