Zazzaɓin Lassa Ya Halaka Mutane 176 A Jihohin Najeriya 21

Hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutum 176 sakamakon cutar zazzaɓin Lassa a faɗin jihohin ƙasar 21 cikin wata 10.

Hukumar ta ɗora alhakin mutuwar kan rashin kai rahoto da wuri, da rashin neman taimakaon likitoci.

Kazalika, ƙarin mutum 955 ne daga cikin 8,367 da aka gwada suka kamu da cutar ta Lassa a 2025, inda jihohin Ondo, Bauchi, Edo, Taraba suka zama cibiyar cutar da kashi 88 cikin 100 na duka mutanen.

Post masu alaƙa

Ƴan sandan Kano za su ƙara ƙaimi wajen amsa kiran gaggawa – CP Bakori

Masu Garkuwa Da Janar Rabe Na Neman A Sako ’Yan Bindigar Da Ke Hannun Gwamnati

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu