Zazzaɓin Lassa Ya Halaka Mutane 176 A Jihohin Najeriya 21

Hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutum 176 sakamakon cutar zazzaɓin Lassa a faɗin jihohin ƙasar 21 cikin wata 10.

Hukumar ta ɗora alhakin mutuwar kan rashin kai rahoto da wuri, da rashin neman taimakaon likitoci.

Kazalika, ƙarin mutum 955 ne daga cikin 8,367 da aka gwada suka kamu da cutar ta Lassa a 2025, inda jihohin Ondo, Bauchi, Edo, Taraba suka zama cibiyar cutar da kashi 88 cikin 100 na duka mutanen.

Post masu alaƙa

Yan bindiga sun sace shugaban ƙaramar hukuma a Zamfara

Yar Najeriya ta kammala jami’ar Burtaniya da daraja ta daya (1st Class) a ilimin kimiyar samar da manhajar kasuwancin zamani.

Gwamnati ta buƙaci jama’a su guji taɓa kumfar da ta ɓulla a hanyar Kaduna-Abuja