Wane horo sojojin Najeriya za su samu daga dakarun Amurka?
Karo biyu a cikin wannan wata na Fabarairun 2026 aka tabbatar da isar dakarun Amurka a Najeriya. A farkon watan ne shugaban dakarun Amurka da ke a nahiyar Afirka (Africom), Dagvin Anderson ya tabbatar da cewa Amurka ta tura wata kwarya-kwaryar tawagar sojin Amurka zuwa Najeriya. Sai kuma ga shi a ranar Litinin shalkwatar tsaro […]









