Labarai

Babban Labari Siyasa

Bukatunmu kan gyaran dokar zaɓen Najeriya – El-Rufai

Gyara ga dokar zabe na ci gaba da tayar da ƙura a Najeriya, inda yan’adawa suka ce tilas ne majalisar dattawan ƙasar ta amince da amfani da na’ura wajen aika sakamakon zabe nan take ta intanet. Tsohon gwamnan Kaduna Malam Nasir El-Rufai kuma jigo a jam’iyyar hamayya ta ADC, ya ce suna son a amince […]

Babban Labari Labarai

Saudiyya za ta zuba jarin biliyoyin Dala a Siriya

Saudiyya ta sanar da wani gagarumin zuba jari a fannin samar da ababen more rayuwa a Syria, a yayin da ta ke jaddada goyon bayanta ga gwamnatin Damascus. Ƙasar Saudiyyar ta sanya kuɗin da ya kai dala biliyan biyu wajen gina sabbin filayen tashi da saukar jirage biyu a birnin Aleppo, da kuma dala biliyan […]

Babban Labari Labarai

Shettima ya kai ziyara Kwara bayan mummunan harin jihar

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya kai ziyarar jaje zuwa jihar Kwara inda mahara suka kashe gomman mutane cikin makon nan. Cikin wata sanarwa da fadarsa ta fitar ta ce Shettima ya kai ziyarar ce bisa umarnin shugaban ƙasar Bola Tinubu. “Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya umarci mataimakinsa ya kai ziyarar jaje jihar da kuma […]

Labarai Siyasa

APC ta naɗa Masari shugaban babban taronta na ƙasa

Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta maye gurbin gwamnan jihar Imo Hope Uzodinma da tsohon gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari a matsayin shugaban kwamitin babban taronta na ƙasa. Babban sakataren jam’iyyar na ƙasa, Surajudeen Basiru ne ya bayyana haka cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X. Jam’iyyar ta saka ranakun 27 […]

Labarai

HAJJ 2026: Gwamna Namadi ya naɗa Sarkin Dutse a matsayin Amirul Hajj

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar A. Namadi, ya amince da naɗa Mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji (Dr) Hamim Muhammad Nuhu Sanusi, a matsayin Amirul Hajjin Jihar Jigawa kuma shugaban tawagar gwamnatin jihar don aikin Hajjin shekarar 2026 mai zuwa. Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa (SSG), Malam Bala […]

Babban Labari Labarai

Yan Jaridun Bauchi mutum 14 sun yi hatsari a bakin aiki

Tawagar ’yan jarida kimanin su 14 da suka fito daga kafafen yaɗa labarai dabam-dabam suka gamu da mummunar hatsarin mota a yayin da suke cikin tawagar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC). Tawagar da suke tafiya a ƙarƙashin jagorancin ƙaramin Ministan Raya Yankuna, Alhaji Uba Maigari Ahmadu a yayin da suke ziyarar buɗewa da […]

Labarai

Gwamna Namadi ya jagoranci babban taron fasaha a Argentina domin bunƙasa noman alfalfa da ci gaban kiwo a Jigawa

Gwamna Namadi ya jagoranci babban taron fasaha a Argentina domin bunƙasa noman alfalfa da ci gaban kiwo a Jigawa. A ƙoƙarinsa na mayar da Jihar Jigawa cibiyar samar da ciyawar kiwo da kasuwancin noma a Najeriya, Gwamna Malam Umar Namadi ya jagoranci wata babbar tawagar kwararru zuwa Jamhuriyar Argentina domin nazarin dabarun ci gaban noma. […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai