Labarai

Babban Labari Labarai

Ƙungiyar ƙwadago ta buƙaci ma’aikatan Abuja su koma aiki

Ƙungiyar ƙwadago ta buƙaci ma’aikatan Abuja su koma bakin aiki bayan cimma matsaya da ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike, biyo bayan taron sulhu da aka gudanar domin warware matsalolin da suka haifar da yajin aikin da ake yi. Taron ya gudana bisa jagorancin shugaban kwamitin majalisar dattawa na Abuja, Sanata Mohammed Bomoi. Sanarwar […]

Babban Labari Labarai

NECO ta saki sakamakon jarrabawar 2025 na dalibai masu zaman kansu

Hukumar Jarrabawa ta Kasa (NECO) ta saki sakamakon jarrabawar dalibai masu zaman kansu na shekarar 2025. Shugaban Hukumar Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya bayyana cewa 93,425 daga cikin daliban sun zana jarrabawar harshen Ingilishi, inda kashi 78.32% (73,167) suka samu akalla Credit. Dalibai 93,330 sun zana jarrabawar Lissafi inda kashi 91.35 % (85,256) suka samu akalla […]

Babban Labari Labarai

Gobara ta tashi a Kasuwar Singa da ke Kano

Gobara ta tashi a Kasuwar Singa da ke birnin Kano a safiyar Litinin ɗin nan. Rahotanni sun nuna cewa ’yan kasuwa da mazauna sun shiga tashin hankali matuƙa sakamakon tashin gobarar a shahararriyar kasuwar kayan abincin kwali da da ke titin Bello Road. ‎An yi asarar dukiyoyi na maƙudan kuɗaɗe a sanadiyyar gobarar ta safiyar […]

Babban Labari Labarai

Sojoji sun kashe ƙasurgumin ɗan ta’adda Gwaska Ɗanƙarami

Sojojin Najeriya sun halaka ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska Ɗanƙarami tare da wasu ’yan ta’adda da dama a Jihar Zamfara. Sojojin rundunar Operation Fansan Yamma sun aika ’yan ta’addan lahira ne a yayin musayar a wata maɓoyar da ’yan bindiga sama da 100 suka taru da nufin ƙaddamar da hare-hare a kama fararen hula da jami’an […]

Babban Labari Labarai

An karrama hukumar NOA da lambar yabo

Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa, NOA, ƙarƙashin jagorancin Darakta-Janar Malam Lanre Issa Onilu, ta samu Lambar Yabo ta Kwarewa a Gyaran Ɗabi’u da Gina Ƙasa. Cibiyar Centre for Positive Value Reorientation and Advocacy ce ta bayar da lambar yabon a yayin ƙaddamar da littafinta “Paradise at a Crossroads,” a NBA Hall, Ilorin. An […]

Babban Labari Labarai

Wasu matasa sun bankawa ɓarawon waya wuta a Ɗorayi

Wasu matasa a unguwar Dorayi dake jihar Kano sun bankawa wani da ake zargin barawon waya ne wuta, bayan da kwace wayar wata mata. Rahotanni sun ce barawon ya chakawa matar wuka a kirjin ta kafin matasan su hallaka shi ta hanyar kone shi da taya. Tuni aka garzaya da matar zuwa asibiti cikin mummunan yanayi […]

Babban Labari Labarai

Sojojin Najeriya sun kashe manyan mayaƙan ISWAP

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Haɗin Kai da ke aiki a yankin arewa maso gabshin Najeriya, sun sanar da nasarar kai wasu munanan hare-hare kan ƙungiyoyin ƴan bindiga da ke addabar yankin. A cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba ya fitar, ya ce bayanan sirri sun tabbatar […]

Babban Labari Labarai

Ba mu da shirin sauke Sarki Sanusi II — Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano ta yi fatali da jita-jitar da ake yaɗawa kan cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf na shirin tsige Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II daga kan mulki bayan sauya sheƙar gwamnan daga Jam’iyyar NNPP zuwa APC mai mulki. Gwamnan ya bayyana haka ne a wata tattaunawa ta musamman da ya yi da Aminiya kan lamarin […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai