Rundunar ƴansanda ta tabbatar da kashe jami’anta 10 a artabu da ƴanbindiga a Kebbi
Rundunar ƴansandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta 10 a wani artabu da ƴanbindiga a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya. Rundunar ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:25 na safiyar Litinin 10 ga watan Agusta, a yankin Rafin Makuku da ke ƙaramar hukumar Sakaba. A sanarwar da kakakin rundunar […]










