Kaduna: Rundunar Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Kashe Wasu ‘Yan Fashin Daji
Rundunar sojin Najeriya da ke jihar Kaduna ta ce ta kashe ‘yan fashin daji biyar tare da ƙwato makamai a wani samame da ta kai dajin Kubusu da kuma tsaunukan Kaso a yankin ƙaramar hukumar Chikun a jihar.