EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC, ta tsare tsohon ministan ƙwadago kuma tsohon gwamnan jihar Anambra, Chris Ngige.

Mai magana da yawun Ngige, Fred Chukwuelobe, ya tabbatar da tsare shi da safiyar ranar Alhamis, bayan wasu rahotanni da aka yaɗa cewa an sace shi.

Chukwuelobe ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa, “Ngige yana tare da EFCC. Ba a sace shi ba.”

Har zuwa yanzu, EFCC ba ta bayyana dalilin tsare Ngige ba amma kuma ana sa ran hukumar za ta fitar da cikakken sanarwa kan tsare shi da binciken da take yi a kansa.

Ngige ya zama mutum na biyu daga cikin tsoffin ministocin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da aka tsare a kwanan nan. Kafin shi, an fara tsare tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami, wanda shima yake hannun EFCC.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Oyo ta saka dokar hana fita a ƙananan hukumomi 10

Majalisar Dattawan Amurka ta kaɗa ƙuri’ar haramta wa Trump yaƙi da Iran

CP Bakori ya umarci dakarun rundunar su ƙara faɗaɗa sintiri da dogaro da bayanan sirri.