NOA Ta Bukaci Masana’antar Fina-finai Ta Inganta Dabi’u Da Martaba Nijeriya.

Hukumar wayar da kan jama’a ta kasa, NOA, ta bukaci kungiyar masu shirya fina-finai data yi amfani da masana’antar wajen inganta dabi’u da al’adu da martaba Nijeriya.

Darktan Janar na hukumar, Mallam Lanre Issa-onilu, ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi mambobin kungiyar reshen babban birnin tarayya Abuja.

Mallam Lanre, ya ce fina-finai suna da tasiri sosai wajen chanja tunani da kuma hada kan kasa , inda ya shaidawa tawagar cewa hukumar NOA na shirin hada kai da masana’antar fina-finan don wayar da kan jama’a cikin shirye-shiryensu na film.

Shugaban masu shirya fina-finai reshen babban birnin tarayya Abuja, Desmond Utomwen, ya yabawa hukumar kan kokarin da take yin a wayar da kan jama’a da inganta dabi’u tare da yin alkawarin hada kai da hukumar don fito da fina-finai da za su wayar da kan yan kasa da suka shafi inganta dabi’u da kishin kasa.

Post masu alaƙa

Tinubu ya isa Kenya don halartar taron ƙoli na Afirka da Faransa

Gwamnati ta tilasta yi wa ɗaliban sakandare gwajin ƙwaya a Najeriya

SDP ta zaɓi Farfesa Sadiq Gombe a matsayin Shugaban Jam’iyya na Ƙasa