Karo biyu a cikin wannan wata na Fabarairun 2026 aka tabbatar da isar dakarun Amurka a Najeriya.
A farkon watan ne shugaban dakarun Amurka da ke a nahiyar Afirka (Africom), Dagvin Anderson ya tabbatar da cewa Amurka ta tura wata kwarya-kwaryar tawagar sojin Amurka zuwa Najeriya.
Sai kuma ga shi a ranar Litinin shalkwatar tsaro ta Najeriya ta tabbatar da isar sojojin Amurka 100 zuwa Najeriya.
Cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron ƙasar ta fitar ta hannun daraktan yada labaranta Manjo Janar Samaila Uba, ta ce tuni rukunin farko na sojojin Amurkan da ya ƙunshi dakaru 100 suka sauka a filin jirgin sama da ke Bauchi a arewa maso gabashin ƙasar.
A makon da ya gabata ne Amurka ta sanar da ahirin tura sojoji 200 zuwa Najeriya domin horas da dakarun ƙasar dabarun yaƙi da ƙungiyar masu tayar da ƙayar baya.