ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Najeriya

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta bayyana cewa dukkan jami’o’in gwamnati kusan 150 da ke ƙarƙashin kulawar ta na iya shiga yajin aiki, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Wannan lamari ya biyo bayan da gwamnati ta musanta cewa ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ASUU, inda ta bayyana takardun da ƙungiyar ke magana a kansu a matsayin shawarwari ne kawai.

Daga ranar Litinin din wannan makon, rassan ASUU daban-daban sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma da ƙungiyar ko kuma a fuskanci yajin aikin da zai shafi ɗalibai kusan miliyan biyu a faɗin ƙasar.

Manyan matsalolin sun haɗa da rashin biyan albashin watanni uku da rabi da aka hana da rashin biyan cikon kuɗin albashi na ƙarin matsayi da rashin sakin kuɗaɗen inganta jami’o’i da sauya sunan Jami’ar Maiduguri, da batun kudin ritaya ga malaman jami’a.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda