Kisan ‘Yan Arewa A Edo: ‘Yan Sa Kai Sun Zata Ɓata Gari Ne; Fred Itua
Sakataren Labarai na Fadar Gwamnatin Edo, Fred Itua ya ta tabbatar da cewa ’yan sa- kai ne suka kai mummunan hari kan waɗansu matafiya ‘yan Arewacin Najeriya, amma binciken farko ya tabbatar da cewa ‘yan sa kan sun zata ɓata gari ne a motar da suka tare.










