Labarai

Babban Labari Labarai

Kotu ta bayar da umarnin a kama jami’in DSS Kirista Ifeanyi Festus, bisa zargin sace yarinya musulma da cin zarafinta.

Wata kotun majistiri dake zamanta a Hadejia jihar Jigawa ta bayar da umarnin kamo wani jami’in hukumar tsaron farin kaya, DSS, mai suna Ifeanyi Festus, bisa zarginsa da sace karamar yarinya da tursasa mata sauya addininta zuwa kiistanci tare da cin zarafinta ta hanyar lalata. A cewar kotun, ana zargin jami’in da sace Walida Sani, […]

Babban Labari Labarai

Gobara ta ƙone dukiyar N15m a Gusau

Gobara ta ƙone dukiya ta kimanin Naira miliyan 15 wadda ta tashi a wata ma’adanar kayan ado da ke unguwar Barakallahu a birnin Gusau na Jihar Zamfara. Wani ganau, Sambo Balarabe, ya ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 8 na dare, bayan wani direban babur da ke wucewa ya hango hayaƙi na tashi […]

Babban Labari Labarai

Hukumar Civil Defense Zata yi bincike kan zargin mutawar matashi a ofishinta dake Kano.

Rundunar tsaro ta Civil Defense reshen jihar Kano, ta ce, za ta yi ƙwaƙƙwaran bincike kan zargin kashe wani matashi mai suna, Halifa Abdullahi, a ofishin rundunar na ƙaramar hukumar Fagge. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SC Ibrahim Idris Abdullahi, ne ya bayyana hakan, a ranar Alhamis, biyo bayan yadda a ka zargi jami’an […]

Babban Labari Labarai

Majalisar Dokokin Ribas ta fara shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara

Majalisar Dokokin Jihar Ribas ta fara shirye-shiryen tsige Gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, lamarin da ya haddasa ruɗani a siyasar jihar. A zaman majalisar na ranar Alhamis, da Kakakin Majalisar, Martins Amaewhule, ya jagoranta, Shugaban Masu Rinjaye, Major Jack, ya karanta takardar zargin da ake yi wa gwamnan bisa aikata manyan laifuka. Ya […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai