Labarai

Babban Labari Labarai

Gwamnatin tarayya ta Amince da tsarin Shirya kaso 70 na fina-finan Katun ga Yara daga gida Nijeriya.

  Gwamnatin Nijeriya ta amince da wani sabon tsari wanda zai tabbatar da ana shirya kaso 70 cinkin 100 na fina-finan wasan yara wato Katun, a wani yunkuri na chusa kishin kasa a zukatan yara. Shugaban hukumar NOA na kasa Mallam Lanre Issa-Onilu, ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da kwamitin mutane bakwai tare da […]

Kungiyar ‘Yan Kasuwa, Masana’antu, Ma’adanai, da Noma ta Kano, KACCIMA, ta ce tana shirin sanyawa cibiyar kasuwanci da taro da sunan Shugaban Kamfanin Dangote Group, Aliko Dangote.
Kasuwanci

Matatar Man Dangote Ta Rage Farashin Fetur Zuwa N699

Matatar man Dangote ta sake rage farashin man fetur ɗin da take sayar da man, inda ta rage farashin man fetur ɗin daga Naira 828 zuwa Naira 699 kan kowace lita. Bayanan farashin da aka wallafa a shafin  kasuwancin farashin man fetur a Petroleumprice.ng a ranar Juma’a sun nuna cewa matatar ta aiwatar da wani […]

Babban Labari Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 3 A Binuwai

Dakarun Sojin Operation Whirl Stroke (OPWS), sun kashe wasu mutum uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, yayin wani samame da suka kai a Ƙaramar Hukumar Ukum, a Jihar Binuwai. Mai magana da yawun OPWS, Laftanar Ahmad Zubairu, ya ce sojojin sun samu bayanan sirri kuma suka yi aiki tare da ’yan sandan […]

Babban Labari Labarai

Kotun Koli ta soke afuwar Maryam Sanda, ta sake tabbatar mata da hukuncin kisa.

Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda bisa samunta da laifin kashe mijinta Bilyaminun Bello. Alƙalan kotun guda huɗu a cikin biyar ne suka tabbatar hukuncin, inda ake yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan watsi da ɗaukaka ƙararta, kamar yadda mai shari’a Moore Adumein ne ya sanar da hukuncin […]

Babban Labari Labarai

Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa

Jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo. Jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar ce a cikin wata sanarwa da sakatarenta yada labaranta na kasa, Kwamared Ini Ememobong, ya fitar. Rahotanni sun ce Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya faɗi a ofishinsa da ke gidan gwamnati, Yenagoa, a ranar Alhamis, […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai