Dalilin Da Ya Sa Muka Ziyarci Obasanjo — Turaki

Shugaban jam’iyyar PDP) na ƙasa, Taminu Turaki, ya bayyana cewa sun kai wa tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, ziyara domin neman shawarwari da goyon baya gabanin zaɓen 2027.

Turaki, wanda ya zama sabon shugaban jam’iyyar PDP kwanan nan, ya ziyarci Obasanjo a garin Abeokuta, da ke Jihar Ogun, tare da wasu manyan shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaban Kwamitin Amintattu, Sanata Adolphus Wabara, da wasu tsofaffin gwamnoni.

Ya ce ziyarar wani ɓangare ne na gabatar da sabon shugabancin jam’iyyar ga tsohon shugaban ƙasar.

Turaki, ya ce jam’iyyar PDP yanzu ta samu haɗin kai kuma ta shirya tsaf domin tunkarar manyan zaɓuka masu zuwa, ciki har da zaɓen gwamna a jihohin Ekiti da Osun.

Shi ma Shugaban PDP na Jihar Ogun, Abayomi Tella, ya ce ziyarar ta ƙara wa mambobin jam’iyyar ƙwarin gwiwa.

Ya ƙara da cewa ’yan Najeriya sun gaji da rashin kyakkyawan shugabanci kuma suna buƙatar sauyi a zaɓen 2027.

Post masu alaƙa

Ƴan sandan Kano za su ƙara ƙaimi wajen amsa kiran gaggawa – CP Bakori

Masu Garkuwa Da Janar Rabe Na Neman A Sako ’Yan Bindigar Da Ke Hannun Gwamnati

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu