Tag: Kano

Babban Labari Labarai

Kashim Shettima ya isa Kano domin karɓar gwamna Abba zuwa APC

Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya isa jihar Kano domin karɓar gwamnan Abba zuwa jam’iyyar APC, a wani muhimmin taron siyasa da ya ja hankalin jama’a. An shirya taron karɓar gwamnan ne a hukumance a filin wasan Sani Abacha Stadium, inda dubban magoya baya da shugabannin jam’iyya suka fara taruwa tun da wuri. Rahotanni sun […]

Babban Labari Labarai

DSS ta kama wanda ya sace yaro dan shekara 5 a Kano

Hukumar  tsaron ta farin kaya (DSS) ta samu nasarar ceto wani yaro mai shekaru biyar, mai suna Muhammad Haruna, daga hannun masu garkuwa da mutane a Kauyen Danzaki, karamar hukumar Gezawa. An gudanar da aikin ceton ne da misalin ƙarfe 7:40 na yamma ranar Alhamis, bayan an sami rahoton cewa an sace yaron kuma masu […]

Babban Labari Labarai

Ƙungiyar mafarauta ta Nijeriya, zata yi zanga-zangar saboda rashin biyan diyya ga iyalan mafarauta da aka Kashe a Uromin Edo

Ƙungiyar mafarauta ta Nijeriya, zata gudanar da zanga-zangar lumana saboda, rashin biyan diyya ga iyalan mafarauta yan asalin jihar Kano, da aka yi wa kisan gilla a Uromin jihar Edo. Akallla mafarauta 16 aka yi wa kisan gilla lokacin da suke hanyarsu ta dawowa gida Kano daga kudancin Nijeriya, lamarin da ya jefa iyalansu cikin […]

Babban Labari Siyasa

APC ta fara faɗawa tarkon rikici a jihar Kano

Kurar rikici ta fara turnuƙewa a jam’iyyar APC mai mulki a jihar Kano, da ke arewacin Najeriya, makonni bayan sauyin sheƙar gwamna Abba Kabir Yusuf. An fara ganin ƙurar ne a tarukan haɗa kan ‘ya’yan jam’iyyar APC tsoffi da sabbi a cikin wasu ƙananan hukumomin jihar. Shugabancin APC ne ya ba da umarnin gudanar da […]

Babban Labari Labarai

Gobara ta tashi a Kasuwar Singa da ke Kano

Gobara ta tashi a Kasuwar Singa da ke birnin Kano a safiyar Litinin ɗin nan. Rahotanni sun nuna cewa ’yan kasuwa da mazauna sun shiga tashin hankali matuƙa sakamakon tashin gobarar a shahararriyar kasuwar kayan abincin kwali da da ke titin Bello Road. ‎An yi asarar dukiyoyi na maƙudan kuɗaɗe a sanadiyyar gobarar ta safiyar […]

Babban Labari Labarai

Wasu matasa sun bankawa ɓarawon waya wuta a Ɗorayi

Wasu matasa a unguwar Dorayi dake jihar Kano sun bankawa wani da ake zargin barawon waya ne wuta, bayan da kwace wayar wata mata. Rahotanni sun ce barawon ya chakawa matar wuka a kirjin ta kafin matasan su hallaka shi ta hanyar kone shi da taya. Tuni aka garzaya da matar zuwa asibiti cikin mummunan yanayi […]

Babban Labari Siyasa

NNPP ta soki masu kiran cewa mataimakin gwamnan Kano ya ajiye aiki

Jam’iyyar NNPP ta yi Alla-wadai da kalaman kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Ibrahim Waiya, wanda ya buƙaci mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo ya ajiye aikinsa. Wata sanarwa da kakakin jam’iyyar a jihar Kano, Ibrahim Karaye ya fitar, ya ce har yanzu kundin tsarin mulki ya bai wa mataimakin gwamnan ci gaba da riƙe […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000