Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Ma’aurata Da Yarinya Mai Shekaru 2 A Katsina

Wasu Gungun yan bindiga sun kai hari, a Sabuwar Unguwa dake jihar Katsina, tare yin garkuwa da wasu ma’aurata da kuma yarsu mai suna Jidda Anas, sannan suka halaka wani jami’in bijilanti.

Rahotanni na cewa yan bindigar sun shiga cikin unguwar da misalin karfe 3:00am na daren ranar talata, inda suka shiga gidan, Anas Ahmadu da matarsa Halimatu wadda take dauke da juna biyu da kuma yarsu Jidda mai shekaru 2.

Jami’in bijilantin mai suna Abdullahi Muhammad, ya rasa ransa ne lokacin da yake kokarin bayar da taimako ga ma’auratan da aka yi garkuwar da su.

Rundunar yan sandan jihar Katsina, ta bakin mai magana da yawun ta, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya tabbatar da cewa sun fara gudanar da bincike kan faruwar lamarin.

Post masu alaƙa

Fursuna ya tsere bayan hatsarin motar jami’ai a Yobe

Katsina ta kafa kotunan tafi da gidan ka don gaggauta hukunta ’yan ta’adda

‘Talauci ya faɗo daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto