Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Shugaban hukumar shigi da fici ta Najeriya mai ritaya kuma jigo a jam’iyyar APC, Muhammad Babandede, ya ziyarci iyalan tsohon ɗan majalisar wakilai, Hon. Abba Anas Adamu Laushi, wanda ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane. Babandede ya bayyana rasuwar marigayin a matsayin babban rashi ga iyalansa, al’ummarsa da kuma abokan siyasarsa, yana mai […]

Read more

Sanata ya bar APC a jajibirin zaɓen fidda gwani a Kebbi 

Sanatan Kebbi ta Kudu a Majalisar Dattawa, Garba Musa Maidoki, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC. A cikin wata wasiƙa da ya aike wa Shugaban APC na mazaɓar Rafin Zuru mai ɗauke da kwanan watan 14 ga Mayu, 2026, Sanatan ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon rikice-rikicen cikin gida da suka dabaibaye jam’iyyar. […]

Read more

An kama ɓarauniyar jariri a asibiti a Zamfara.

An kama wata matashiya ’yar shekara 27, kan zargin satar jariri mai kwana 10 da haihuwa a Babban Asibitin Ƙaura Namoda da ke Jihar Zamfara. Dubun wadda ake zargin ya cika ne kwanan da sace jaririn, inda ’yan sanda suka fara gudanar da bincike bayan samun rahoton. Bayanan samun ƙorafin ne Babban Ofishin ’Yan Sanda […]

Read more

Yusuf Buhari ya lashe zaɓen takarar majalisar tarayya a APC

Yusuf Buhari, ɗan tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari, ya samu nasara a zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC na mazabar Sandamu/Daura/Mai’adua. Da yake bayyana sakamakon zaɓen, shugaban kwamitin zaɓe na mazabar, Lawan Garba, ya ce Yusuf Buhari ya samu ƙuri’u 17,342, inda ya doke abokin takararsa, Auwalu Musa Daura, wanda ya samu ƙuri’u […]

Read more

Man City ta lashe kofin FA bayan doke Chelsea 1-0

Ƙungiyar ƙwallon kafa ta Manchester City ta lashe kofin FA na shekarar 2026 bayan doke Chelsea 1-0. Antoine Semenyo ne ya zura ƙwallon da ta bai wa Man City nasara bayan an dawo daga hutun rabin lokaci. Wannan ne kofi na biyu da ƙungiyar ta lashe a kakar wasa ta bana bayan lashe kofin Carabao […]

Read more

Adadin ɗabilan da aka sace daga Borno sun kai 50

Bayanan da ke fitowa daga Najeriya na cewa fiye da ɗalibai 50 ne aka bayar da rahoton garkuwa da su a wasu hare-hare da aka kai wa makarantu a yankin arewa maso gabashin ƙasar aranar Juma’a Rahotonni na cewa mafi yawan yaran ƴan tsakanin shekara biyu zuwa biyar ne, waɗanda aka sace daga makarantun nazare. […]

Read more