Labarai

Babban Labari

Kwamishinan ƴan sandan Kano CP Ibrahim Bakori ya gargaɗi masu cin zarafin mutane a shafukan sada zumunta.

Kwamishinan ƴan sandan jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa aikin tsaro da al’umma ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta tsaro da zaman lafiya jihar. CP Bakori, ya bayyana hakan ne a ci gaba da bikin ranar ƴan sandan Nijeriya ta shekarar 2026, tare da yin aiyukan hidimtawa al’umma a sassa dabam-daban na jihar. […]

Babban Labari

Tinubu ya nemi majalisa ta amince ya ƙara naira tiriliyan 9 cikin kasafin kuɗin 2026

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya nemi Majalisar Dokokin Ƙasa ta amince da ƙara naira tiriliyan 9 a cikin kasafin kuɗin shekarar 2026, wanda hakan zai ɗaga jimillar kasafin daga naira tiriliyan 58.4 zuwa naira tiriliyan 67.4. An bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta a zaman majalisa […]

Babban Labari

Gwamnan Bauchi Na Shirin Sauya Sheka Zuwa ADC

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana shirinsa na sauya sheka zuwa Jam’iyyar ADC, inda ya ce jam’iyyar na da damar kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a zaben 2027. Idan Bala Mohammed ya sauya shekar, ADC ta samu gwamna mai ci na farko, wanda hakan zai kara mata karfi a kan tsofaffin gwamnoni da tsofaffin […]

Babban Labari

Ƴan majalisar wakilai 8 na Kano sun fice daga NNPP zuwa APC

Ƴan Majalisar Wakilai takwas daga Jihar Kano sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar NPP zuwa jam’iyyar APC, lamarin da ya ƙara girgiza siyasar jihar. Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ne ya sanar da sauya sheƙar a hukumance yayin zaman majalisar a yau Talata, bayan karanta wasiƙun da ‘yan majalisar suka aike wa zauren. A cikin […]

Babban Labari

NOA ta ƙaddamar da manhajar ClheeanMobile App don ƙarfafa hulɗa tsakanin gwamnati da jama’a

Hukumar wayar da kan jama’a ta ƙasa (NOA) ta ƙaddamar da wata sabuwar manhajar waya mai suna CLHEEAN Mobile App, wadda aka tsara domin ƙarfafa hulɗa tsakanin gwamnati da al’umma tare da rage gibi a harkokin mulki. Daraktan Janar na hukumar, Malam Lanre Issa-Onilu, ya bayyana cewa manhajar za ta bai wa ‘yan Najeriya damar […]

Babban Labari

El-Rufai ya sake gurfana a kotun Kaduna

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya sake gurfana a gaban Babbar Kotun Jihar Kaduna a ranar Talata kan tuhumomin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa (ICPC) ta shigar a kansa. An gurfanar da El-rufai ne kan laifuka da suka hada da amfani da mukami ba bisa ka’ida ba, damfara, da bai wa […]

Babban Labari

Komawar Kwankwaso ADC barazana ce ga APC

Mai fashin baƙi akan al’amuran yau da kullum a Nijeriya, Ibrahim Sadauki Kabara, ya bayyana cewa komawar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, jam’iyar ADC babbar barazana ce ga jam’iyyar APC a Kano dama ƙasa baki ɗaya. Komawar Kwankwaso, wanda shi ne tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai